Wani jami’in Hamas ya gaya wa BBC cewa wataƙila ƙungiyar ta riƙa ɓoye sunayen sababbin shugabanninta saboda dalilai na tsaro.
A shekara ta 2003 ma ƙungiyar ta yi hakan bayan kisan gillar da Isra’ila ta yi wa tsohon shugabanta Sheikh Ahmed Yassin da kuma wanda ya gaje shi, Dr Abdel Aziz al-Rantisi.
Ƙungiyar ta tsara zaɓen sabon shugabanta a watan Maris na shekara mai zuwa, to amma kafin sannan wani kwamitin mutum biyar ne zai riƙa gudanar da ita.
Kwamitin zai ƙunshi Khalil al-Hayya, da Khaled Meshaal, da Zaher Jabarin, da Muhammad Darwish, shugaban majalisar magabata – Shura – da kuma mutum na biyar wanda ba a bayyana shi ba.
Jami’in ya nuna cewa Khalil al-Hayya shi ya karɓi yawancin ɗawainiyar siyasa da harkokin waje, ƙari a kan gudanar da harkokin Gaza.
Saboda wannan ɗawainiya da yake ggudanarwa kusan a yanzu shi ne ke aiki kamar shugaban ƙungiyar.