Kungiyar Tagwaye ta kasa reshen jihar Kano ta gudanar da zaben shugabaninta karo na farko wanda za su jagoranci akalar ƙungiyar.
Shugaban kwamitin gudanar da zaben, Hassan Isah Muhd Gwale wanda ya jagoranci zaɓen ya tabbatar da Injiniya Hássan Ahamad Makari a matsayin sabon shugaban kungiyar, sai kuma Hassan Auwal Muhd Jak City ya zama mataimakin shugaba, yayin ds Hussaini Kabir Minjibir ya kasance a matsayin sakataren kungiyar.
Yayin ganawa da manema labarai, Hassan Isa Gwale ya bukaci wadanda su ka samu nasarar da su yi aiki tukuru, domin ciyar da kungiyar gaba.
Ya kuma bukaci wadanda basu samu nasara a zaben ba, da su marawa wadanda suka samu nasarar, domin ciyar da kungiyar gaba.
An dai gudanar da zaben ne a makarantar gidan Makama da ke ƙwaryar birnin jihar Kano, inda tagwaye mata da maza daga ƙananan hukumomi arba’in da hudu su ka halarci zaben.
Sabbin shugabannin dai a na sa ran za su tafiyar da harkokin kungiyar dai-dai da yadda kundin tsarin mulkin kungiyar ya tsara.
A Jawabinsa bayan rantsuwar kama aiki sabon shugaban kungiyar Tagwayen, Injiniya Hassan Ahmad Makeri, ya ce za su yi aiki tukuru tare da bujiro da sabbin dabarun da za su ciyar da kungiyar Tagwayen Kano gaba.