fidelitybank

Za mu cigaba da zanga-zanga saboda Tinubu ba shi da biyar magance matsalar mu – Ƙungiya

Date:

Ƙungiyar ‘The Take it Back Movement’, ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka shirya zanga-zagar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce ”zanga-zangar za ta ci gaba”, duk kuwa da kiran dakatar da ita da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya yi.

Cikin jawabin da ya gabatar wa ƙasar ranar Lahadi da safe, shugaba Tinubu ya yi kira ga waɗanda suka shirya zanag-zangar su dakatar da ita tare da rungumar hanyar tattaunawa.

To sai cikin wani saƙo da ƙungiyar ‘The Take it Back Movement’ ta wallafa a shafinta na intanet, ta ce shugaban bai taɓo buƙatunsu cikin jawabin nasa ba, sannna ya kasa ɗaukar alhakin ”kisan gillar da aka yi wa masu zanga-zangar”.

Ƙungiyar kare haƙƙin bil-adama ta Amnesty International ta ce mutum 13 jamai’an tsaro suka kashe ranar Alhamis.

To sai rundunar ‘yansandan ƙasar ta musanta amfani da ƙarfin da ya wuce kima kan masu zanga-zangar, tana mai cewa mutum bakwai ne kawai suka mutu.

Rundunar ‘yansandan ta kama kusan mutum 700.

A ranar Lahadi wasu mutane da ake zargin ɓata-gari ne sun tarwatsa masu zanga-zangar a birnin Legas da ke kudancin ƙasar.

Masu zanga-zangar na buƙatar gwamnati ta mayar da tallafin man fetur da ta cire domin rage farashin fetur da na lantarki, haka kuma suna buƙatar hukumomin ƙasar su magance matsalar tsaro da cin hanci da rashawa.

Ana sa ran ci gaba da zanag-zangar a faɗin ƙasar har zuwa ranar Asabar mai zuwa.

Shugaban ƙasar dai ya umarci jami’an tsaro su ci gaba da tabbatar da doka da oda.

Yayin da ake fargabar samun ƙarin arangama tsakanin masu zanga-zangar da jami’an tsaro.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...
X whatsapp