fidelitybank

Za mu cigaba da yi wa Lebanon luguden wuta – Isra’ila

Date:

Isra’ila ta ce za ta cigaba da kai hare-hare kudancin Lebanon duk da kiraye-kirayen da shugabannin duniya suke yi a Babban Taron MDD na a tsagita wuta.

 

Ma’aikatar Lafiyar Lebanon ta ce an samu ƙarin mutuwar mutum shida a daren Talata, inda jimillar waɗanda suka rasu ya kai 560, tun bayan kaddamar da hare-hare da luguden wutar da Isra’ila ta fara ranar Litinin.

 

Isra’ila da Hezbollah sun tabbatar da kashe Ibrahim Qubaisi – wanda kwamandan Hezbollah ne da ya jagoranci harba makaman roka zuwa Isra’ila – ranar Talata.

 

Dubban ‘yan Lebanon ne suka tsere daga muhallansu tare da neman mafaka a makarantu da sansanonin da gwamnati ta samar.

 

Ofishin kare haƙƙin ɗan Adam na Majalisar Ɗinkin Duniya ya nuna damuwar kan adadin mutanen da aka kashe, inda ya ce akwai alamar yin watsi da dokokin aikin agaji na duniya.

 

A bangare guda Isra’ila ta nanata cewa dole ya sa take kai hare-hare a yankunan da ke da ɗimbin farar hula kamar Beirut, saboda Hezbollah na amfani da mutane a matsayin garkuwa.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp