Isra’ila ta ce za ta cigaba da kai hare-hare kudancin Lebanon duk da kiraye-kirayen da shugabannin duniya suke yi a Babban Taron MDD na a tsagita wuta.
Ma’aikatar Lafiyar Lebanon ta ce an samu ƙarin mutuwar mutum shida a daren Talata, inda jimillar waɗanda suka rasu ya kai 560, tun bayan kaddamar da hare-hare da luguden wutar da Isra’ila ta fara ranar Litinin.
Isra’ila da Hezbollah sun tabbatar da kashe Ibrahim Qubaisi – wanda kwamandan Hezbollah ne da ya jagoranci harba makaman roka zuwa Isra’ila – ranar Talata.
Dubban ‘yan Lebanon ne suka tsere daga muhallansu tare da neman mafaka a makarantu da sansanonin da gwamnati ta samar.
Ofishin kare haƙƙin ɗan Adam na Majalisar Ɗinkin Duniya ya nuna damuwar kan adadin mutanen da aka kashe, inda ya ce akwai alamar yin watsi da dokokin aikin agaji na duniya.
A bangare guda Isra’ila ta nanata cewa dole ya sa take kai hare-hare a yankunan da ke da ɗimbin farar hula kamar Beirut, saboda Hezbollah na amfani da mutane a matsayin garkuwa.