fidelitybank

Za mu cigaba da tunkudo da man fetur zuwa kasuwar duniya – OPEC

Date:

Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur da ƙawayenta ta OPEC+ ta amince da ci gaba da rage yawan gangar mai miliyan biyu daga kasuwar duniya duk rana.

Ƙungiyar ta sanar da matakin a yau Lahadi bayan kammala taronta karo na 34 ta bidiyo, wanda ministocin ƙasashen suka halarta.

Matakin na zuwa ne kwana ɗaya bayan ƙasashen ƙungiyar G7 – mafiya girman tattalin arziki a duniya – sun ƙayyade farashin dala 60 kan kowace ganga ɗaya na man Rasha.

A ganawar da suka yi kafin yanzu, OPEC+ ta amince ta rage yawan man daga kasuwa da ganga miliyan biyu a kullum duk da kiraye-kirayen da Amurka ta dinga yi na kar ta yi hakan.

Ƙungiyar mai mamba 13 ta ce ba za ta janye matakin ba, “wanda aka ɗauka bayan lura da kasuwar a lokacin don ɗaukar matakin da ya zama dole da zimmar daidaita kasuwar fetur a duniya”.

OPEC ta sha nanata cewa ba za ta ɗauki ɓangare ba a yaƙin da Rasha, wadda mamba ce, take yi da Ukraine tana mai cewa ba ƙungiyar siyasa ba ce.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...
X whatsapp