fidelitybank

Za mu cigaba da tunkudo da man fetur zuwa kasuwar duniya – OPEC

Date:

Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur da ƙawayenta ta OPEC+ ta amince da ci gaba da rage yawan gangar mai miliyan biyu daga kasuwar duniya duk rana.

Ƙungiyar ta sanar da matakin a yau Lahadi bayan kammala taronta karo na 34 ta bidiyo, wanda ministocin ƙasashen suka halarta.

Matakin na zuwa ne kwana ɗaya bayan ƙasashen ƙungiyar G7 – mafiya girman tattalin arziki a duniya – sun ƙayyade farashin dala 60 kan kowace ganga ɗaya na man Rasha.

A ganawar da suka yi kafin yanzu, OPEC+ ta amince ta rage yawan man daga kasuwa da ganga miliyan biyu a kullum duk da kiraye-kirayen da Amurka ta dinga yi na kar ta yi hakan.

Ƙungiyar mai mamba 13 ta ce ba za ta janye matakin ba, “wanda aka ɗauka bayan lura da kasuwar a lokacin don ɗaukar matakin da ya zama dole da zimmar daidaita kasuwar fetur a duniya”.

OPEC ta sha nanata cewa ba za ta ɗauki ɓangare ba a yaƙin da Rasha, wadda mamba ce, take yi da Ukraine tana mai cewa ba ƙungiyar siyasa ba ce.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp