fidelitybank

Za mu cigaba da luguden wuta a kan ‘yan bindiga – Sojojin Sama

Date:

Wata majiya a jihar Zamfara ta bayyana cewa, mabiyan sarakunan ‘yan fashi irin su Bello Turji, Halilu Buzu da Adamu Aleiru na sake haduwa domin sake kai wani hari bayan kashe irinsu sama da 40 a kauyukan Malele da Mutunji na masarautar Dansadau a jihar Zamfara.

Majiyar ta shaida wa DAILY POST cewa an ga yaran Halilu Buzu a kan hanyar Dunkurmi a kan hanyarsu ta zuwa yankin Malele, yayin da ’yan kungiyar Adamu Aleiru aka gansu a unguwar Year Gada da ke kan iyaka tsakanin Dansadau da Gusau, babban birnin Jihar.

Idan dai za a iya tunawa, a tsakanin makon jiya zuwa ranar Litinin ne ‘yan bindigar suka addabi wasu kauyuka, musamman al’ummar Malele da Mutunji na masarautar Dansadau a karamar hukumar Maru ta jihar.

Bayan tashin hankalin, Rundunar Sojan Sama da na kasa da ke aiki da Operation Hadarin Daji sun tunkari ‘yan bindigar a wani samame da suka yi da ‘yan bindigar inda aka ce sun yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga sama da 40 da ke kan babura a Malele.

An kai harin ne a ranar Asabar din da ta gabata a lokacin da sojojin saman Najeriya da sojojin kasa na sojojin Najeriya suka kai farmaki kan ‘yan ta’addan a wani samame na hadin gwiwa da suka yi da juna, kamar yadda majiya ta bayyana.

Majiyar sojan ta ce ayyukan sojojin Najeriya da sojojin saman Najeriya (NAF) na samun sakamako mai kyau a yankin inda aka kashe ‘yan bindiga da dama a yakin.

‘Yan bindigan da ke kokarin tserewa daga harin da sojojin sama, suka kai musu a wani karamin kauye da ake kira Mutunji domin samun mafaka.

A cewar daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojin saman Najeriya Air Commodore Edward Gabkwrt, an girke jami’an sojin sama a dukkan wurare masu mahimmanci kuma a shirye suke su yaki ‘yan fashin.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp