fidelitybank

Za mu cigaba da biyan ma’aikata Naira dubu 35 – Gwamnatin Tarayya

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, za ta ci gaba da biyan tallafin N35,000 da ta fara biyan ma’aikata domin rage radadin illar cire tallafin man fetur ga ma’aikatan ƙasar.

Gwamnatin ta kuma roki kungiyar kwadagon kasar da su janye yajin aikin da suka shirya yi na kwanaki 14.

Karamar ministar Kwadago ta Najeriya, Nkeiruka Onyejeocha ce ta bada wannan tabbacin a Abuja a wajen wani taro da shugabannin ƙungiyoyin kwadagon biyu da aka yi kan wa’adin da suka bai wa gwamnati na tafiya yajin aiki idan ba ta cika musu bukatunsu ba a cikin makonni biyu.

An dai cimma yarjejeniyar ne ranar 2 ga Oktoba, 2023 mai dauke da abubuwa 16 da suka hada da ƙarancin albashin ma’aikata da tallafin naira 35,000 ga ma’aikata duk wata da dai sauransu.

Onyejeocha ta kuma ce gwamnati ta kara kaimi wajen ganin an kammala aiwatar da wannan yarjejeniya.

Ministar ta kira taron ne domin bayyana wa ƙungiyoyin kwadagon yadda ake aiwatar da yarjejeniyar, da kuma jaddada aniyar gwamnati kan yarjejeniyar.

“Gaskiya ne da cewa mun kulla yarjejeniya, amma gwamnati ta nuna gaskiya kan wannan batu, kuma bisa la’akari da gaggawar lamarin ne na kira wannan taro domin tattaunawa ita ce hanya mafi dacewa a kodayaushe, kuma dukkan mu muna neman lafiya kasancewar mutanenmu.”

Ta yi nuni da cewa, yayin da martanin kungiyoyin kwadagon kan gazawar gwamnati na cika yarjejeniyar bai dace ba, yana da kyau ayi la’akari da cewa wasu abubuwa da ke cikin yarjejeniyar ba za a iya cim musu ba a lokaci guda.

Rahotanni sun ce an tashi daga taron ba tare da cimma wata matsaya ba dangane da bukatun.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp