Majalisar dokokin jihar Ondo, ta ce, za ta ci gaba da yunƙurinta na tsige mataimakin gwamnan jihar, Lucky Aiyedatiwa duk da ƙarar da ya shigar a kotu na neman a dakatar da batun.
Aiyedatiwa ya garzaya babbar kotu ne da ke Akure, inda ya buƙaci da a dakatar da ƴan majalisar daga yunƙurin tsige shi.
Sai dai a wata sanarwa da ta samu sa hannun shugaban majalisar dokokin jihar, Oladiji Olamide Adesanmi, majalisar ta tabbatar wa al’ummar jihar cewa, za ta ci gaban da bin matakin har ƙarshe, sai dai duk da haka za ta bi matakan da kundin tsarin mulkin ya gindaya.
Sanarwar ta ce “majalisar ba za ta yi watsi da nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata na binciken masu riƙe da muƙaman gwamnati ba, musamman a inda ake batu na manyan zarge-zarge aikata rashawa da tozarta matsayi, kamar yadda ake yi wa mataimakin gwamnan.”