Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da kare muradun ‘yan Najeriya a duk inda suke.
Shugaban ya bayyana haka ne yayin da aka fara kwashe ‘yan Najeriya a kasar Ukraine.
A cewar Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasa, Buhari ya yi magana a ranar Alhamis, a birnin Nairobi na kasar Kenya, a wani taro da kungiyar ‘yan Najeriya mazauna kasar.
Ministan harkokin waje Geoffrey Onyeama ne ya wakilci shugaban a wajen taron.
“A namu bangaren gwamnati, za mu ci gaba da kare muradun ‘yan Nijeriya a duk inda suke. Mun nuna hakan a cikin lokaci, saboda mun sami dalilin kwashe ‘yan kasarmu ta hanyar cutarwa a kasashen waje,” in ji shi.
“Mun yi hakan a Libya, Afirka ta Kudu kuma yanzu mun fara yin hakan a Ukraine, inda dubban ‘yan kasarmu, musamman dalibai, ke cikin tarko sakamakon yakin da ke tsakanin Rasha da Ukraine.”
Shugaban ya yabawa ‘yan Najeriya mazauna Kenya bisa hadin kan da ke tsakaninsu.