Babbar hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC, ta ce tana aiki da wasu hukumomin ƙasar a wani sabon yunƙuri na ɓullo da hanyoyin ƙarfafa gwiwar matasa.
Ta ce tana yin hakan ne baya ga ƙoƙarin wayar da kai da ilimantar da matasa game da hanyoyin neman kuɗi na halaliya a intanet maimakon aikata laifukan intanet da za su iya kai mutum cikin wahala da ɗauri da kuma da-na-sani.
Shugabar sashen wayar da kai da inganta halayya ta EFCC, Hajiya A’isha Mohammed ce ta bayyana haka a wani ɓangare na bikin Ranar Ƴaƙi da Rashawa ta Duniya.
Ana gudanar da bikin ne duk rana irinta yau 9 ga watan Disamba.
Taken ranar a bana shi ne “Haɗa kai da Matasa Wajen Yaƙi da Cin Hanci: Kyautata Halin Ƙwarai domin Gobe.”