fidelitybank

Za mu biya ƙarin albashin dubu 25 – Gwamnatin Tarayya

Date:

Gwmanatin tarayya ta ce, za ta ci gaba da bai wa ma’aikatan ƙasar ƙarin albashin wucin gadi na naira 25,000 a kowane wata har zuwa lokacin da za a kammala cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashi a ƙasar.

Cikin wani jawabi da ya yi wa manema labarai ranar Asabar a Abuja, ministan yaɗa labaran ƙasar, Mohammed Idris ya ce wa’adin mafi ƙarancin albashi da aka yi a shekarar 2019 ya ƙare ne ranar, 8 ga watan Afrilun 2024.

A ranar juma’a ne dai ƙungiyoyin ƙwadogon ƙasar suka ce za su tsunduma yajin aiki daga gobe Litinin, kasancewar wa’adin ranar 31 ga watan Mayu da suka bai wa gwamnati na amincewa da mafi ƙarancin albashi ya wuce ba tare da cimma matsaya ba.

Gwamnatin ta ce amince da biyan naira 60,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ƙasar, to amma haɗakar ƙungiyoyin ƙwadagon ƙasar sun yi watsi da wannan ƙari, inda suka buƙaci gwamnati ta biya raira 494,000 a matsayin mafi ƙarancin albashin.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne dai shugaban ƙasar ya yi wata ganawa da jagororin gamayyar ƙungiyoyin ƙwadagon bayan da suka yi barazanar shiga yajin aiki kan matakin shugaban na cire tallafin man fetur.

A lokacin ganawar shugaba Tinubu ya yi musu alƙawura da dama ciki har da amincewa da ƙarin albashin wucin gadi na Naira 25,000 ga kowane ma’aikaci, har tsawon wata shida, kafin cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashi.

Kan haka ne ministan yaɗa labaran ya ce kasancewar har yanzu ba a kammala cimma matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashin ba, gwamnati za ta ci gaba da bayar da wannan ƙari har zuwa lokacin da za a cimma matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashin.

”Alƙwarin gwamnatin tarayya na yi wa ma’aikata ƙari a albashinsu na wata shida, ba zai dakata ba har sai an kammala cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashi”, in ji ministan

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta ɓullo da wannan tallafi ga ma’aikatan ƙasar ne domin tabbatar da cewa ba su galabaita ba, kafin cimma matsaya a kan mafi ƙarancin albashin.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp