fidelitybank

Za mu binciki zafin wariyar launin fatar da aka yi wa Lamine – Real Madrid

Date:

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta buɗe bincike kan cin zarafin wariyar launin fata da ake zargin an yi wa matashin ɗan wasan Barcelona, Lamine Yamal, a wasan El-Clasico da aka buga ranar Asabar a Bernabeu.

Bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna wani bangare na magoya bayan Madrid suna furta kalamun ɓatanci kan ɗan kasar Sifaniyan mai shekaru 17 da haihuwa yayin da yake murnar ƙwallon da ya ci a minti na 77.

Sanarwar da Real Madrid ta fitar ta ce: “Real Madrid ta yi kakkausar suka ga duk wani nau’in halayya da ya shafi nuna wariyar launin fata, da kyamar baƙi ko tashin hankali a fagen ƙwallon ƙafa da wasanni, kuma ta yi matukar baƙin cikin cin mutuncin da wasu tsirarun magoya bayan ƙungiyar suka yi a daren asabar a wani ɓangare na filin wasan.”

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Sifaniya (RFEF) da La Liga sun ɗauki matakai don magance ƙaruwar cin zarafin wariyar launin fata wanda suka haɗa da rufe wani ɓangare na filin wasa.

A makon da ya gabata, an kama wasu mutane huɗu bisa zarginsu da gudanar da wani gangami a shafukan intanet domin nuna ƙyama da wariyar launin fata a kan ɗan wasan Real Madrid Vinicius Jr.

Haka kuma an yanke wa wasu magoya bayan Valencia uku hukuncin ɗaurin watanni takwas a gidan yari a watan Yuni. saboda cin zarafin ɗan wasan gaban na Madrid a wani wasa a watan Mayun 2023.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp