fidelitybank

Za mu binciki zafin wariyar launin fatar da aka yi wa Lamine – Real Madrid

Date:

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta buɗe bincike kan cin zarafin wariyar launin fata da ake zargin an yi wa matashin ɗan wasan Barcelona, Lamine Yamal, a wasan El-Clasico da aka buga ranar Asabar a Bernabeu.

Bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna wani bangare na magoya bayan Madrid suna furta kalamun ɓatanci kan ɗan kasar Sifaniyan mai shekaru 17 da haihuwa yayin da yake murnar ƙwallon da ya ci a minti na 77.

Sanarwar da Real Madrid ta fitar ta ce: “Real Madrid ta yi kakkausar suka ga duk wani nau’in halayya da ya shafi nuna wariyar launin fata, da kyamar baƙi ko tashin hankali a fagen ƙwallon ƙafa da wasanni, kuma ta yi matukar baƙin cikin cin mutuncin da wasu tsirarun magoya bayan ƙungiyar suka yi a daren asabar a wani ɓangare na filin wasan.”

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Sifaniya (RFEF) da La Liga sun ɗauki matakai don magance ƙaruwar cin zarafin wariyar launin fata wanda suka haɗa da rufe wani ɓangare na filin wasa.

A makon da ya gabata, an kama wasu mutane huɗu bisa zarginsu da gudanar da wani gangami a shafukan intanet domin nuna ƙyama da wariyar launin fata a kan ɗan wasan Real Madrid Vinicius Jr.

Haka kuma an yanke wa wasu magoya bayan Valencia uku hukuncin ɗaurin watanni takwas a gidan yari a watan Yuni. saboda cin zarafin ɗan wasan gaban na Madrid a wani wasa a watan Mayun 2023.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp