fidelitybank

Za mu binciki tuhumar da kasar Nijar ta ke yi wa Najeriya – Majalisa

Date:

Majalisar dattawa ta ba da umurnin binciken zarge zargen da shugaban mulkin sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani ya yi na cewa gwamnatin Najeriya na haɗa kai da Faransa wajen kawo cikas ga tsaron ƙasarsa.

Umurnin na zuwa ne bayan wani ƙuduri da shugaban kwamitin tsaro na majaliar, Sanata Shehu Buba ya gabatar, inda ya jaddada cewa babban abin damuwa shi ne yadda Tchiani ya zargi mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, da tsohon shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta ƙasa, Ahmed Rufai, da hannu dumu-dumu wajen yi wa ƙasarsa bita-da-ƙulli.

Cikin zarge-zagen nasa, Tchiani ya ce gwamnatin Najeriya na taimaka wa ƙungiyar ƴan ta’adda ta Lakurawa da ke arewa maso yammacin ƙasar, wajen kafa sansanoni a Sokoto da Zamfara da kuma Kebbi, sannan suna amfani da wasu sansanonin sojoji a Najeriya domin kai hari kan bututun man Nijar da kuma kawo barazanar tsaro a ƙasarsa.

A martaninsa a zaman majalisar, mataimakin shugaban majalisar, sanata Barau Jibrin wanda ya jagoranci zaman ya amince da matsayar da ta buƙaci kwamiti kan tsaron ƙasar da kwaminitin harkokin ƙasashen waje su gudanar da bincike su kuma gabatar da rahoton nan da makonni huɗu.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp