fidelitybank

Za mu bincika ƙorafin da ake yi kan rubuta sakamakon bogi a zaɓen Edo – INEC

Date:

Hukumar zaɓe INEC, ta ce za ta binciki zargin rubuta alƙaluman da ba na gaskiya ba a wasu rumfunar zaɓen gwamnan jihar Edo da aka hudanar ranar Laraba.

Cikin wata sanarwa ta hukumar ta fitar a shafinta na X, ranar Asabar da daddare, INEC ɗin ta sha alwashin gudanar da cikakken bincike kan zargin shigar da alƙaluman sakamakon da ba na gaskiya a takardar rubuta sakamako a wasu rumfunan za ben jihar.

“Wannan shi ne karo na biyu da muke samun irin wannan ƙorafi a cikin rumfunan zaɓe 4,519 da aka gudanar da zaɓen. Don haka hukumarmu za ta ɗauki matakin bincike cikin gaggawa kan lamarin, tare da ɗaukar mataki kan duk wanda aka samu da hannu a ciki,’’ kamar yadda sanarar ta yi ƙarin haske.

A yanzu dai hankula sun karkarta birnin Benin, babban birnin jiran inda ake jiran dakon fara karɓar sakamakon zaɓen daga ƙanannan hukumomin jihar 18.

Bayanai da aka tattara daga rumfunan zaɓe na nuna cewa ‘yan takara biyu na PDP mai mulkin jihar da APC mai mulkin Najeriya ne ke kankankan a zaɓen.

Shi dai ɗan takarar PDP na samun goyon bayan gwamnan jihar, yayin da na APC ke samun goyon bayan tsohon gwamnan jihar kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasar.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp