fidelitybank

Za mu bi kadin kisan da aka yi wa ɗalibin Najeriya a Canada – Gwamnati ta

Date:

Gwamnatin tarayya ta sha alwashin bin kadin kisan da aka yi wa wani dalibi dan Najeriya mai shekara 19 da ke karatu a kasar Canada. Rahotanni sun bayyana ana zargin ‘yan sandan Canada ne sukai ajalin matashin.

Shugaban hukumar kula da ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (Nidcom) Abike Dabiri-Erewa, ta bayyana zargin kisan dalibin a Manitoba a Canada da rashin imani.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar 4 ga watan Junairu 2024, dauke da sa hannun maimagan da yawun ofishin Abike ta ce za su tabbatar an yi wa mamacin adalci.

Sanarwar ta kara da kira ga hukumomin kasar Canada da tuni suka ce sun fara gudanar da bincike kan lamari su ta bbatar an yi shi cikin adalci.

Sun mika sakon ta’aziyya ga iyaye da ‘yan uwa da aboakan dalibi Folabi, tare da fatan Allah ya sa bakin wuyarsa kenan.

Yadda Folade ya gamu da ajalinsa

Kamar yadda Nidcom ta fitar da sanarwa, bayanan da suka samu sun nuna dan sanda ne ya harbi matashin dan Najeriya mai shekaru 19 a ranar 31 ga watan Disamba 2023, gabannin shiga sabuwar shekarar 2024 a yankin Manitoba da ke Canada.

Duk da cewa babu cikakkun bayanai kan mutuwarsa, amma hukumar ‘yan sandan Monitoba sun wallafa takaitaccen bayani a shafinsu na intanet na cewa ” sun ce an kira ‘yan sandan ta wayar tarho, akan wani matashi da ya ke abu kamar maras hankali.”

‘Yan sandan sun ce su na isa wurin, duk kokarin da suka yi domin shawo kan matashin ya ci tura, dalilin da ya sa ‘yan sandan sukai harbi kenan bisa tsautsayi ya yi ajalinsa.”

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp