fidelitybank

Za mu bayyana ranar da ba za mu shiga aji ba – ASUU

Date:

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ce, za ta ayyana ranar da ba za ta shiga aji ba a jami’o’in ƙasar domin bayyana rashin jin daɗinsu game da zargin da take yi wa gwamnatin tarayya na riƙe musu albashin wasu watanni.

Babban jami’in ƙungiyar mai lura da shiyyar Kano Farfesa Abdulkadir Muhammad ya shaida wa BBC cewa ƙungiyar ASUU ta yanke shawarar ne domin bayyana ɓacin ranta kan matakin da gwamnatin tarayya ta ɗauka na ƙin biyan mambobin ƙungiyar albashinsu na wasu watanni bayan sun janye yajin aiki.

Ya ce ”kowane reshe zai zaɓi rana guda da zai gudanar da taro tare da zanga-zangar lumana, domin nuna ɓacin ransu da rashin jin daɗinsu kan yadda gwamnatin tarayya ke ƙoƙarin mayar da malaman jami’o’i ma’aikatan wucin gadi”.

Ya ƙara da cewa ”ASUU za ta gudanar da taro a kowane reshe na ƙungiyar, inda kuma duka mambobin ƙungiyar za su hallara, bayan gabatar da laccoci a wajen taron, mambobin ƙungiyar za su gudanar da zanga-zangar lumana a cikin kowacce jami’a, sannan kuma a ranar ba za su shiga aji domin koyawa dalibai karatu ba’

A cikin watan Oktoba ne ASUU ta janye yajin aikin da ta kwashe wata takwas tana gudanarwa.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp