fidelitybank

Za mu bayar da mamaki a ɓangaren tsaro – Matawalle

Date:

Sabon ƙaramin ministan tsaro, Muhammad Bello Matawalle, ya ce, shi da takwaransa ministan tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, za su bai wa maraɗa ƙunya a ɓangaren samar da tsaro a Najeriya.

Yayin da yake jawabi a wani taron liyafa da aka shirya masa don taya shi murnar samun matsayin a Abuja, Matawalle ya ce ya yi ta jin bayanai ana ta cewa shi da Badaru ba su da ƙwarewar da za su iya magance matsalar tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Tsohon gwamnan na jihar zamfara ya ce masu faɗin wannan magana ba su ma san me ake nufi da tsaro ba.

”To ba a nan gizo ke saƙar ba, domin kuwa za ka iya haifar ɗa, amma ya fi ka ƙwazo, ya fi ka hazaƙa, sannan ya fi ka ilimi”.

Matawalle ya ce a lokacin da yake gwamnan jihar Zamfara babu abin da bai yi ba, domin daƙile matsalar tsaron da jihar ke fuskanta, inda ya ce an kwashe lokaci mai tsawo ba tare da samun labarin faruwar wani abu na tayar da hankali a jihar ba.

Ƙaramin ministan tsaron ya ce ya ɓullo da matakai da dabarun yaƙi da ‘yan bindiga a lokacin da yake gwamnan jihar ta Zamfara.

”Duk matakan da na riƙa ɗauka domin magance matsalar tsaro a zamfara, sai na yi wasu gwamnoni su ɗauka”.

Bello Matawalle na daga cikin ministocin da za su fuskanci babban ƙalubale a ma’aikatunsu, sakamakon yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a ƙasar, kama daga ayyukan ‘yan fashin daji a arewa maso yamma, da Boko Haram a arewa maso gabas, ga kuma matsalar ‘yan awaren IPOB a yankin kudu maso gabashin ƙasar.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp