Sojojin Jamhuriyar Nijar, sun yi barazanar kashe hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum, idan har aka samu shiga tsakani na soji daga kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ta ECOWAS.
Kamfanin dillacin labarai na Associated Press a ranar Alhamis ya ruwaito cewa, wasu “Jami’an Yammacin Turai” biyu sun bayyana cewa, masu saka hannun jari sun ba da wannan barazanar yayin da suke magana da wani babban jami’in diflomasiyyar Amurka.
Rahotanni sun ce, shugabannin sojojin sun yi wannan barazanar ne jim kadan kafin ECOWAS ta ba da umarnin aike da rundunar da za ta maido da mulkin dimokradiyya a Nijar.
Kasashen duniya na fafutukar ganin an warware rikicin shugabancin kasar cikin lumana.