Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya buƙaci al’ummomin da ƴan bindiga su ka yi wa kisan gilla a Jihar Zamfara, da su ƙara haƙuri cewa za su gano waɗanda su ka aikata wannan mummunan aiki tare da ɗaukar mataki mai tsauri a kansu.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu ya fitar, ya ce, Buhari ya nuna ɓacin ransa matuƙa dangane da rahoton da ya samu kan kisan gillan da a ka yi, inda ya ce shure-shure ne ƴan bindigan su ke yi wanda bai hana su mutuwa, ganin cewa suna fuskantar matsin lamba daga sojoji waɗanda a ka inganta da makamai, domin yaƙar ƴan bindigar.
Shugaba Buharin ya sake tabbatar da cewa, “Ƴan bindigar na daf da zama tarihi a Najeriya, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba a yaƙin da mu ke yi da waɗannan mutanen da su ka addabi jama’ar da ba su ji ba su gani ba”. Buhari
Jihar Zamfara dai fama da hare-hare daga harin ƴan ta’adda, domin kuwa ko a kwanan nan ƙananan hukumomin Anka da Bukuyyum da ke Jihar su ka tabbatar da binne mutum 143 sakamakon harin da ya rutsa da su.