fidelitybank

Za mu ɗauki mataki mai tsauri a kan masu kisan gilla a Zamfara – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya buƙaci al’ummomin da ƴan bindiga su ka yi wa kisan gilla a Jihar Zamfara, da su ƙara haƙuri cewa za su gano waɗanda su ka aikata wannan mummunan aiki tare da ɗaukar mataki mai tsauri a kansu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu ya fitar, ya ce, Buhari ya nuna ɓacin ransa matuƙa dangane da rahoton da ya samu kan kisan gillan da a ka yi, inda ya ce shure-shure ne ƴan bindigan su ke yi wanda bai hana su mutuwa, ganin cewa suna fuskantar matsin lamba daga sojoji waɗanda a ka inganta da makamai, domin yaƙar ƴan bindigar.

Shugaba Buharin ya sake tabbatar da cewa, “Ƴan bindigar na daf da zama tarihi a Najeriya, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba a yaƙin da mu ke yi da waɗannan mutanen da su ka addabi jama’ar da ba su ji ba su gani ba”. Buhari

Jihar Zamfara dai fama da hare-hare daga harin ƴan ta’adda, domin kuwa ko a kwanan nan ƙananan hukumomin Anka da Bukuyyum da ke Jihar su ka tabbatar da binne mutum 143 sakamakon harin da ya rutsa da su.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp