fidelitybank

Za mu ɗauki mataki mai tsauri a kan masu kisan gilla a Zamfara – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya buƙaci al’ummomin da ƴan bindiga su ka yi wa kisan gilla a Jihar Zamfara, da su ƙara haƙuri cewa za su gano waɗanda su ka aikata wannan mummunan aiki tare da ɗaukar mataki mai tsauri a kansu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu ya fitar, ya ce, Buhari ya nuna ɓacin ransa matuƙa dangane da rahoton da ya samu kan kisan gillan da a ka yi, inda ya ce shure-shure ne ƴan bindigan su ke yi wanda bai hana su mutuwa, ganin cewa suna fuskantar matsin lamba daga sojoji waɗanda a ka inganta da makamai, domin yaƙar ƴan bindigar.

Shugaba Buharin ya sake tabbatar da cewa, “Ƴan bindigar na daf da zama tarihi a Najeriya, ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba a yaƙin da mu ke yi da waɗannan mutanen da su ka addabi jama’ar da ba su ji ba su gani ba”. Buhari

Jihar Zamfara dai fama da hare-hare daga harin ƴan ta’adda, domin kuwa ko a kwanan nan ƙananan hukumomin Anka da Bukuyyum da ke Jihar su ka tabbatar da binne mutum 143 sakamakon harin da ya rutsa da su.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp