fidelitybank

Za a yi zaben Benue a ranar Talata – INEC

Date:

Hukumar zaɓe INEC, ta ce, sai a gobe ne za ta gudanar da zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun jiha a ƙaramar hukumar Kwande ta jihar Benue.

A wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita, ta ce a baya ta ɗage zaɓen da aka tsara gudanarwar ranar Asabar 18 ga wata, bayan da aka samu cuɗanyar muhimman takardun zaɓe tsakanin gundumomin majalisar dokokin jiha biyu da ke ƙaramar hukumar.

Kan haka ne hukumar ta ce ta tuntuɓi wakilan jam’iyyu da sauran masu ruwa da tsaki domin sake sanya sabuwar ranar da za a gudanar da zaɓen.

Karanta Wannan: INEC na kokarin murde zaben Adamawa – Atiku

Sanarwar ta ƙara da cewa bayan tuntuɓar masu ruwa da tsaki a yanzu hukumar ta saka gobe Talata 21 ga watan Maris a matsayin ranar da za a gudanar da zaɓen a ƙaramar hukumar.

Daga ƙarshe hukumar ta yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a a yankin da su fito domin zaɓar mutanen da suke so a zaɓen da za a gudanar goben.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp