fidelitybank

Za a yi jana’izar sarki Olubadan na 42

Date:

Anjima a yau Juma’a ne za a yi jana’izar sarki Olubadan na 42 a birnin Ibadan da ke jihar Oyo.

Sarki Olubadan na Ibadan, Oba Olalekan Balogun ya mutu ƴan kwanaki bayan ya yi bikin cikarsa shekara biyu kan karaga.

Kakakin Sarkin, Dele Ogunsola ne ya tabbatar da mutuwarsa a ranar Alhamis.

Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde shi ma ya tabbatar da mutuwar sarkin yana shekara 81 a wata sanarwa da ya fitar.

Gwamna Makinde ya bayyana cewa sarkin wanda shi ne Olubadan na 42 ya mutu ne a asibitin koyarwa na jami’ar UCH da ke jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya.

Gwamna Makinde ya bayyana sarkin a matsayin mutumin da ya cimma nasarori da dama da suka zama ci gaba ga Ibadanland cikin shekara biyun da ya yi yana mulki.

“Babban bango ya faɗi; Sarki Dakta Balogun ya rasu,” in ji gwamna Makinde.

Kola Balogun, wanda ƙani ne ga sarkin ya ce za a yi jana’izar sarkin a gidansa da ke Aliiwo, kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

Wane ne marigayi Sarki Olubadan na 42?

Marigayi sarki Oba Olalekan Balogun ɗan siyasa ne, ɗan kasuwa kuma tsohon sanata.

An haife shi a Balogun cikin watan Oktoban 1942.

Balogun ya taɓa zama mamba a hukumar gudanarwar manyan kamfanoni da dama a Najeriya da ƙasashen waje, musamman a ɓangaren man fetur da noma da kasuwanci da shugabanci da yawon buɗe ido.

Ya kuma taɓa riƙe muƙamai da dama a kamfanin mai na Shell.

Ya yi karatu a jami’ar Columbus International da jami’ar Brunel da kuma jami’ar Manchester – dukkansu a Birtaniya.

A fagen siyasa, Balogun tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a Najeriya a ƙarƙashin jam’iyyar SDP.

Ya kuma taɓa yi wa PDP takarar gwamna a jihar Oyo.

Daga bisani, Balogun ya zama sanata a Najeriya. In ji BBC.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp