fidelitybank

Za a yi jana’izar ƴan wasa da ma’aikata 19 na jihar Kano da suka mutu bayan sun dawo daga wasan ƙasa

Date:

Motar da ke ɗauke da ƴanwasan Kano da masu horar da su a gasar wasanni ta ƙasa wato National Sport Festival ta Najeriya ta yi hatsarin a hanyar komawa gida, inda rahotanni suka ce mutum 19 daga cikinsu sun rasu, sannan wasu sun jikkata.

Lamarin ya faru kimanin kilomita 50 zuwa Kano a yau Asabar bayan motar ta taso daga jihar Ogun da ke kudu maso yammacin ƙasar bayan an kammala wasannin a ranar Juma’a.

Ibrahim Umar Fage shugaban riƙo na hukumar wasanni ta jihar Kano ya tabbatar wa BBC da aukuwar lamarin, inda ya ce, “ƴanwasanmu sun kwana a Abuja ne da safe sai suka kama hanyar komawa gida. A kusa da Dakatsalle suka yi hatsari. Motar ta faɗa wata gada da ke kusa da Ciromawa. Aƙalla mutum 19 zuwa 20 ne suka rasu, akwai wasu kuma a asibiti,” in ji shi.

Shi ma Kwamishinan matasa da wasanni na jihar, Mustapha Rabiu Kwankwaso ya bayyana kaɗuwarsa kan hatsarin, inda ya ce lamari ne da ya taɓa jihar baki ɗaya.

A wata sanarwa da kwamishinan ya fitar, ya ce “wannan lamarin abin tayar da hakali ne matuƙa. Muna jajanta wa ƴanuwa da iyalan waɗanda suka rasu da ma mutanen jihar Kano baki ɗaya,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ɗauki ɗawainiyar kula da sauran waɗanda suka ji raunuka.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp