Hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, ta ce za a wallafa sakamakon zaɓe daga rumfunan zaɓen gwamna a jihar Bayelsa da Kogi da kuma Imo a shafin intanet na hukumar da ake wallafa sakamakon zaɓe.
Hukumar zaɓen ta sanar da hakan ne a wata sanarwa da fitar a ranar Alhamis.
Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ya yi alƙawarin samar da yanayi na bai ɗaya ga dukkan ƴan takara.
Ya ce hukumar ba ta goyon bayan wani ɗan takara a zaɓen gwamnan da za a yi a jihohin Bayelsa da Imo da kuma Kogi.
Ya kuma yi alƙawarin shirye-shiryen ma’aikatan hukumar, yana mai cewa, sun dage da tabbatar da cewa jami’an sun isa wurin zaɓen suna jiran masu kaɗa kuri’a maimakon masu kaɗa kuri’a su je suna jiran isowarsu.
Sanarwar ta ce “Wannan shi ne karo na farko a tarihin mu da ake gudanar da waɗannan zaɓuka a rana guda a faɗin shiyoyin siyasar ƙasar guda uku da suka haɗa da jihar Kogi da ke arewa ta tsakiya, da Imo da ke kudu maso gabas, da kuma Bayelsa da ke kudu maso kudu.”
INEC ta ce ta kammala tura kayan zaɓe da suka haɗa da na’urar tantance masu zaɓe (BVAS) da kuma sauran muhimman kayayyaki.