fidelitybank

Za a tantance mutane 8 a matsayin Kwamishinonin jihar Ribas

Date:

‘Yan majsalisar dokokin Rivers da ke biyayya ga gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, za su tantance mutane takwas da gwamnan ya aika sunayensu, domin naɗa su kwamishinoni.

A wata wasika da akawun majalisar, Dr. G, N Gillis-West, ya aika, a jiya Litinin ya gayyaci mutanen da su bayyana a zaurn majalisar a yau Talata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Wasikar ta nuna cewa, majalisar karkashin jagorancin shugabanta na bangaren da ke biyayya ga gwamnan, Victor Oko-Jumbo, na sa ran tantance mutanen zuwa karfe goma na safe.

Wannan shi ne karo na biyu da bangaren majalisar da ke biyayya ga Fubara zai tantance mutanen da za a nada kwamishinoni tun bayan da majalisar ta rabu biyu – masu biyayya ga gwamna da kuma masu biyayya ga tsohon gwamnan jihar kuma ministan Abuja Nyesom Wike.

A makon da ya gabata ne majalisar bangaren masu biyayya ga Gwamna Fubara ta tantance tare da tabbatar da babban lauya Dagogo Iboroma (SAN) a matsayin sabon babban lauyan gwamnatin jihar kuma kwamishinan sharia, bayan da Farfesa Zaccaeus Adangor, (SAN), wanda ke biyayya ga Wike ya sauka daga wannan mukami, sakamakon sabanin da ya ya tsananta tsakanin gwamnan da tsohon mai gidansa na siyasa.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp