Hukumomin abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya, sun yi gargaɗin matsananciyar yunwa ga ƙasashe 16 a cikin watanni masu zuwa.
Sun ce yankunan Falasɗinawa da Sudan da Sudan ta Kudu da Mali da Haiti za su fi fuskantar matsalar.
Sauran ƙasashen da matsananciyar yunwar za ta iya ta’azzara sun haɗa da Najeriya da Chadi da Yemen da Mozambique da Myanmar da Syria da kuma Lebanon.
Rikice-rikice ne babban abin da ke haddasa yunwar ko kuma ya ba da gudunmowa cikin halin da ƙasashen suka sa mu kansu.