fidelitybank

Za a shafe tsawon lokaci a kan layi kafin a ga gawar Sarauniya

Date:

Ministar Al’adu a Birtaniya Michelle Donelan ta yi gargadin cewa za a iya samun dogayen layuka fiye da yadda aka yi tsammani don ganawa da gawar Sarauniya Elizabeth II a babban zauren Westminster.

Ta ce akwai yiwuwar samun dogayen layuka na dubban masu ta’aziyya, da ka iya shafe awa 30 a kan layi.

A kan haka ta gargadi al’umma da su shirya jure wa tsayuwa ta tsawon awanni a kullum, su kuma shirya jure wa yanayi.

Sai dai ta ce ”Gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa ta tabbatar jama’ar da za su yi balaguro zuwa London ba su samu matsala ba.”

Ms Donelan ta ce sama da mutum 1,000 ne a kullum za su kasance a inda jama’a suka yi layi don su taimaka masu.

Ta kara da cewa kamfanonin Tate Modern da Shakespeare Globe za su haska ofisoshinsu da ke London da hoton Sarauniya Elizabeth, sannan shaguna za su raba abin sha ga jama’a.

Bugu da kari an tanadi ban-daki guda 500 a kan hanyar da ke sa zauren na Westminster don biyan bukatar jama’a.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin Æ´an Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp