Hukumar kula da yanayi ta kasa Nimet, ta yi hasashen samun hazo da kura ta kwanaki 3, daga yau litinin zuwa ranar laraba a sassan kasarnan.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar lahadi a Abuja, tace lamarin zai shafi arewacin kasar nan da arewa ta tsakiya inda za a fuskanci kura da kuma hazo.
Hakazalika kudancin kasar nan zai fuskanci hazo, a don haka sanarwar ta shawarci masu Ababan hawa da suyi tuki cikin nutsuwa.
Ranar Talata za a sami hazo, sai kuma a ranar Laraba hazon zai mamaye arewacin kasar nan.
Sanarwar ta shawarci kamfanonin jiragen sama da su lura da wannan gargadi, tare da yin aiki da hukumar domin kaucewa hadari.