fidelitybank

Za a samu ambaliyar ruwa a Abuja – FEMA

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin Tarayya FEMA, ta yi gargaɗin samun ruwan sama mai karfi gaske da zai iya haifar da ambaliya a babbar birnin ƙasar Abuja da wasu jihohin ƙasar a ranakun Asabar da Lahadi.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Juma’a mai ɗauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar Nkechi Isa, ya ce hukumar na gargaɗin ne bayan da hukumar kula da yanayi ta ƙasar ta yi hasashen samun ruwan sama mai ƙarfin gaske haɗe da iska da ambaliya da zaizayewar ƙasa a wasu sassan jihohin Katsina da Kano da Bauci da Plateau da Taraba da kuma Abujan

Hukumar kula da yanayi ta kasar NiMET ta yi hasashen cewa za a samu ambaliya ruwa tare da batsewar koguna da iska mai ƙarfi, da zaizaiyewar ƙasa da walkiya da kuma tsawa.

Hukumar ta NiMET ta yi kira a sauya matsugunai ga al’umomin da suke cikin hatsarin fuskantar ambaliyar, wadda za ta iya lalata dukiyoyi tare da haifar da cutattuka.

Babban daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin Abuja Dakta Abbas Idriss ya ce hukumar ta sanya jami’anta cikin shirin ko-ta-kwana don fuskantar matsalar.

Haka kuma ya yi kira ga mazauna birnin da su riƙa la’akari da gargadin da hukumar ta fitar, tare da kaucewa yin tuƙi ko tafiya a ƙafa a lokacin da ake tsaka da ruwan sama, tare da kauce wa titunan da ruwan zai iya mamayewa.

Ya kuma nemi jama’a da su yi gaggawar tuntuɓar hukumar idan suna buƙatar taimakon gaggawa daga gareta.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp