fidelitybank

Za a rufe tashoshin mota ba bisa ƙa’ida ba a Abuja

Date:

Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja (FCTA) ta ce, za ta rufe duka tasoshin motar da ke aiki ba bisa ƙa’ida ba, a wani mataki na yaƙi da masu fakewa a matsayin direbobi domin yi wa fasinjoji fashi a mota da aka fi sani da ‘One -Chance’.

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai.

An samu rahotannin yin fashi da garkuwa da mutane a Abuja tsawon makonni, inda mazauna birnin ke cikin fargaba kan ayyukan ’yan ta’addan da ke fakewa da sana’ar haya don kai hari da kuma yi wa mutane fashi.

Gidan talabijin na Channels ta ruwaito cewa Wike ya ce hukumar FCTA ta kafa rundunar hadin gwiwa kan laifukan da suka shafi kan iyakoki, tare da mai da hankali kan magance ‘yan fashi da makami.

Ministan ya danganta ƙaruwar aikata laifukan da tasoshin motan da ke aiki ba bisa ka’ida ba da kuma gine-ginen da ba a kammala ba waɗanda ke zama mafakar ɓata-garin.

Ya ƙara da cewa, babban birnin tarayya Abuja a tsakiyar jahohin Neja da Kogi da Nasarawa da kuma Kaduna, inda ake fama da matsalar ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

Mista Wike ya ce, akwai buƙatar rushe gine-ginen da ba a kammala ba da masu laifi ke amfani da su, domin fatattakar ɓata-garin.

Ministan ya jaddada muhimmancin yin la’akari da illolin tsaro a yayin da ake magance matsalolin da suka shafi tasoshin mota ba bisa ka’ida ba.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp