fidelitybank

Za a rufe ma’aikatu hudu a Abuja sabod rantsar da Tinubu

Date:

Hukumomi a Najeriya za su hana shiga da fita a kewayen Sakatariyar Gwamnatin Tarayya da ke tsakiyar birnin Abuja tsawon kwana huɗu saboda bikin rantsar da Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Kazalika, jami’an tsaro za su kulle ma’aikatar harkokin wajen ƙasar tun daga ranar Juma’a, 26 har zuwa Talata, 30 ga watan Mayu.

“Ba za a ƙyale ma’aikata da masu ziyara su shiga ma’aikatun ba har sai Talata, 30 ga wata. lokacin da za a ci gaba da ayyuka cikin gaggawa,” a cewar wata sanarwa da ofishin kula da ma’aikatan gwamnatin tarayya ya fitar a jiya Juma’a.

A ranar Litinin, 29 ga watan Mayu ne za a rantsar da Bola Tinubu na jam’iyyar APC mai mulki, inda zai jagoranci ƙasar tsawon shekara huɗu bayan ya yi nasara a zaɓen watan Fabarairu da ya gabata.

Sai dai jam’iyyar PDP da ɗan takararta Atiku Abubakar na ƙalubalantar sakamakon zaɓen a kotu, suna masu cewa an tafka maguɗi. Ita ma Labour Party ta Peter Obi ta shigar da ƙara.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp