fidelitybank

Za a rufe karɓar kuɗin aikin Hajji a Kano

Date:

Hukumar kula da alhazai ta jihar Kano ta yi kira ga maniyyata da suka kai kuɗin ajiya a wani ɓangare na zuwa hajjin bana, su kammala biyan kuɗinsu daga nan zuwa ranar 21 ga wannan wata.

Tun da farko, hukumar alhazan ta buƙaci maniyyatan su cika kuɗin tafiyarsu zuwa naira miliyan biyu da rabi kafin Hukumar kula da Aikin Hajji ta Najeriya ta sanar da haƙiƙanin farashi.

A ranar Juma’a ne, Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa ta sanar da kuɗin tafiya aikin hajjin bana, inda Kano ta faɗa cikin jihohin da za su biya N2,919,000.00.

Da yake jawabi ga manema labarai ranar Asabar, Babban Sakataren Hukumar Alhazai ta Kano, Alhaji Mohammad Abba Dambatta, ya ce nan ba da jimawa ba za a rufe karɓar kuɗin tafiya aikin hajjin.

Ya ce maniyyatan Kano za su biya sama da naira miliyan biyu da dubu ɗari tara ne saboda tashin farashin dalar Amurka da ƙarin haraji daga Saudiyya da kuma kamfanonin sufurin jiragen sama

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp