Hukumar kula da alhazai ta jihar Kano ta yi kira ga maniyyata da suka kai kuɗin ajiya a wani ɓangare na zuwa hajjin bana, su kammala biyan kuɗinsu daga nan zuwa ranar 21 ga wannan wata.
Tun da farko, hukumar alhazan ta buƙaci maniyyatan su cika kuɗin tafiyarsu zuwa naira miliyan biyu da rabi kafin Hukumar kula da Aikin Hajji ta Najeriya ta sanar da haƙiƙanin farashi.
A ranar Juma’a ne, Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa ta sanar da kuɗin tafiya aikin hajjin bana, inda Kano ta faɗa cikin jihohin da za su biya N2,919,000.00.
Da yake jawabi ga manema labarai ranar Asabar, Babban Sakataren Hukumar Alhazai ta Kano, Alhaji Mohammad Abba Dambatta, ya ce nan ba da jimawa ba za a rufe karɓar kuɗin tafiya aikin hajjin.
Ya ce maniyyatan Kano za su biya sama da naira miliyan biyu da dubu ɗari tara ne saboda tashin farashin dalar Amurka da ƙarin haraji daga Saudiyya da kuma kamfanonin sufurin jiragen sama