Wata kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wani mutum da ya kashe ‘ya’yan cikinsa tagwaye.
Wannan na zuwa ne shekaru 5 bayan da mutumin ya kashe yaran nasa, lamarin da ya kai zuwa ga kotu, domin shari’ar.
The Nation ya bayyana yadda mutumin ya tursasawa kansa kashe ‘ya’yan nasa.
Kotun ta jihar Cross River ta samu mutumin laifin dumu-dumu wadda ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wani Anyabime Festus Udo, bisa laifin kashe ‘ya’yansa mata tagwaye guda biyu.
Festus Udo tun a shekarar 2017, ya sanya wa ‘yan matan, Mfoniso Anyanime da Emediong Anyanime guba a abin sha, ya na mai da’awar cewa, su mayu ne kuma sune silar wahalarsa.