Emmanuel Macron zai sha rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasar Faransa a karo na biyu a yau Asabar, bayan nasarar tazarce kan mulki da ya yi a zaben watan da ya gabata.
Sai dai rahotanni na nuna cewa, yanayin da ake ciki a yanzu a Faransa ba zai bada damar bukukuwa ba, don haka Bikin da za a gudanar a fadar shugaban ta Elysee, za a takaita wasu shagulgula da aka saba gani a baya kamar irinsu faratin sojoji, musamman saboda zarcewa zai yi da mulkin.
Mahalarta taron za su saurari jawabin da zai gabatar wanda ake sa ran Mista Macron din zai zayyana manufofinsa.
Ana sa ran nan ba da jimawa ba zai sanar da sabon Firaminista, domin sake kintsa jam’iyyarsa da ke mulki kafin zaben ‘yan majalisa da ke tafe a wata mai kamawa. In ji BBC.