fidelitybank

Za a kawo ƙarshen matsalar tsaro a watan Disamba – Aregbesola

Date:

Rauf Aregbesola, ministan harkokin cikin gida, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa, za’a kawo karshen rashin tsaro a kasar nan a watan Disamba.

Aregbesola ya bayar da wannan tabbacin ne a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Abuja.

A cewar Aregbesola, Buhari ya ce ba zai bar kasar nan ba tare da takaitawa da magance matsalolin tsaro yadda ya kamata ba.

Ministan ya ce Buhari ya baiwa jami’an tsaro wa’adin watan Disamba domin su dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan sassan kasar nan.

“Ya ba da wa’adin kawo karshen irin wannan barazana ga tsaro na rayuka da dukiyoyi kafin watan Disamba.

“Na yi imanin cewa babu wanda ke hutawa a dukkan hannun gwamnati tare da wanzar da doka da oda, tabbatar da tsaro da kawar da barazana.

“Muna kan haka, kuma a matakin farko, dole ne mu tambayi kanmu cewa, mulki shine tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi.

“Za mu kawar da duk matsalolin rashin tsaro nan da Disamba.

“Idan ka dubi yadda al’amura ke gudana a Najeriya, zan gaya maka cewa an samu ci gaba da dama a cikin shekaru,” in ji shi.

Aregbesola ya tuna cewa kafin shekarar 2015 ‘yan Najeriya na zaune da bama-bamai a ko’ina.

Ministan, ya ce gwamnati ta kawar da abubuwan da ke faruwa na bama-bamai, kuma ‘yan Najeriya ba su da irin wannan fargaba.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp