Hukumomin Saudiyya sun zartar da hukuncin kisa kan wasu mutane uku da aka samu da laifin ta’addanci.
Biyu daga cikin wadanda aka yankewa hukuncin kisa ƴan Saudiyya ne, ɗayan kuma ɗan kasar Yemen ne wanda aka bayyana a matsayin ɗan Houthi da ke yaki da ƙawancen da Saudiyya ke jagoranta tsawon shekaru.
Ma’aikatar harkokin cikin gida ta Saudiyya ta ce ɗaya daga cikin mutanen mamba ne na wata ƙungiyar ƴan ta’adda, da aka samu da makamai da abubuwan fashewa a gidansa.
An samu ɗayan ɗan kasar Saudiyya da laifin hannunsa a kisan wani mai gadi.
An zargi ɗan kasar Yemen da shiga Saudiyya ba bisa ƙa’ida ba da nufin kai hare-haren ta’addanci.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun sha suka kan yadda ake gudanar da shari’a a Saudiyya