fidelitybank

Za a kammala aikin titin Abuja zuwa Kano a naira biliyan 280 cikin wata 14 – Minista

Date:

Ministan ayyuka Sanata David Umahi, ya ce, gwamnati za ta rinƙa biyan kamfanin Julius Berger naira biliyan 20 a duk wata, domin kammala aikin sashen kilomita 82 na titin Abuja zuwa Kano, tsawon wata 14 nan gaba.

Ministan wanda ya bayyana haka a yayin ganawa da kamfanin domin sake duba dukkanin kwangilolin tituna da kamfanin ke yi, ya nuna damuwarsa kan ƙarancin kuɗi don kammala ayyukan da gwamnatinsu ta gada.

A game da titin na Abuja zuwa Kano, ministan ya buƙaci kamfanin da ya tsaya a kan aikin ɓangare ɗaya na titin, bayan ya kammala sai ya koma ɗaya ɓangaren.

Ministan ya kuma umarci kamfanin na Berger da cewa nan da mako uku ya cike dukkanin ramukan da ke titin da duwatsu domin magance matsalar rashin kyawun hanyar da masu motoci ke fama da ita.

Kamfanin ya kasa ragowar aikin gida huɗu kuma ya yi alƙawarin kammalawa duka cikin wata 14.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a wata sanarwa da, jami’in yaÉ—a labarai na ministan, Orji Uchenna Orji, ya fitar, ya ce ayyukan titunan sun haÉ—a da na Abuja zuwa Kaduna zuwa Zaria zuwa Kano, da kashi na biyu na titun Legas zuwa Ibadan da Gadar Anacha ta biyu, sai kuma gadojin da ke jihar Legas – Gadar Third Mainland, da Gadar Iddo da kuma Gadar Carter.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp