Ministan ayyuka Sanata David Umahi, ya ce, gwamnati za ta rinƙa biyan kamfanin Julius Berger naira biliyan 20 a duk wata, domin kammala aikin sashen kilomita 82 na titin Abuja zuwa Kano, tsawon wata 14 nan gaba.
Ministan wanda ya bayyana haka a yayin ganawa da kamfanin domin sake duba dukkanin kwangilolin tituna da kamfanin ke yi, ya nuna damuwarsa kan ƙarancin kuɗi don kammala ayyukan da gwamnatinsu ta gada.
A game da titin na Abuja zuwa Kano, ministan ya buƙaci kamfanin da ya tsaya a kan aikin ɓangare ɗaya na titin, bayan ya kammala sai ya koma ɗaya ɓangaren.
Ministan ya kuma umarci kamfanin na Berger da cewa nan da mako uku ya cike dukkanin ramukan da ke titin da duwatsu domin magance matsalar rashin kyawun hanyar da masu motoci ke fama da ita.
Kamfanin ya kasa ragowar aikin gida huɗu kuma ya yi alƙawarin kammalawa duka cikin wata 14.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a wata sanarwa da, jami’in yaÉ—a labarai na ministan, Orji Uchenna Orji, ya fitar, ya ce ayyukan titunan sun haÉ—a da na Abuja zuwa Kaduna zuwa Zaria zuwa Kano, da kashi na biyu na titun Legas zuwa Ibadan da Gadar Anacha ta biyu, sai kuma gadojin da ke jihar Legas – Gadar Third Mainland, da Gadar Iddo da kuma Gadar Carter.