fidelitybank

Za a kammaa gwajin matatar fetur ta Fatakwal a watannan – NNPCL

Date:

Kamfanin mai na Najeriya, NNPCL ya ce a cikin watan nan ne za a kammala gwajin matatar mai ta Fatakwal da ke kudancin ƙasar don ci gaba da aikin tace mai bayan shafe shekaru biyar a rufe.

Kakakin kamfanin Femi Soneye ya ce “nan ba da daɗewa bane za a kammala gwajin matatar don tabbatar da tana aiki yadda ya kamata. Za a kammala a cikin wannan watan.”

Matatar wadda ake inganta ta, za ta soma tace gangar mai 60,000 duk rana kuma kamfanin na NNPCL yana sa ran nan gaba a shekarar, za ta riƙa tace ganga 210,000 ta mai kowace rana.

Matatar man ta Patakwal ɗaya ce daga matatun mai na gwamnati da suka shafe tsawon shekaru a durƙushe wanda kuma a yanzu gwamnatin ke son farfaɗo da ita da nufin kawo karshen dogaron da ƙasar ke yi kan tataccen man da ake shigowa da shi daga wasu ƙasashe.

Ana ganin idan matatar man ta soma aiki, za ta taimaka wajen samuwar man fetur a kasar tare da sauƙaƙa wa ƴan ƙasar wahalhalun da suke fuskanta ta dalilin rashin iya tace man a ƙasar.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp