fidelitybank

Za a janye jami’an tsaron da su ke baiwa manyan jami’an gwamnati kariya

Date:

Najeriya na shirin janye jami’an ‘yan sanda masu bai wa manyan jami’an gwamnati tsaro bisa umarnin shugaban kasa, kamar yadda karamar ministar harkokin ‘yan sanda, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta sanar.

Ta bayyana irin kalubalen da rundunar ‘yan sandan ke fuskanta sakamakon rashin kula da su na tsawon shekaru, wanda ke kawo mata cikas wajen sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya dora mata.

A ci gaba da kokarin da shugaban kasa ya yi na ganin an farfado da aikin ‘yan sanda mai inganci, Sulaiman-Ibrahim ta jaddada buƙatar ‘yan sanda su daidaita tare da inganta ayyukansu.

Ta bukaci cikakken nazari kan cibiyoyin horarwa don dacewa da tsarin aiwatar da doka na zamani da ka’idojin ƙasashen duniya.

Ta yi wannan jawabi ne a wani taron kwana biyu da ‘yan sanda suka gudanar a Abuja.

Ta ce ma’aikatar tana da muhimman a wajen “haɓaka da aiwatar da ingantaccen rahoton sake fasalin ‘yan sanda da kuma yin gyaran fuska ga aikin ‘yan sanda, tare da aiwatar da umarnin shugaban ƙasa kan janye jami’an ‘yan sanda daga ayyukan tsaron ƴan siyasa don haɓaka dabarun aikin ɗan sanda na al’umma”.

Wadannan tsare-tsare na da nufin kawo sauyi da inganta harkokin tsaron cikin gida a Najeriya

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp