fidelitybank

Za a iya shafe shekaru 4 ana gwabzawa a fadan Ukraine da Rasha – Boris

Date:

Shugabannin ƙasashen yamma sun yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a shafe shekara huɗu ana gwabza yaƙi a Ukraine inda suka ce akwai buƙatar a samu agaji mai ɗorewa domin kare ƙasar daga mamayar Rasha.

Firaiministan Birtaniya Boris Johnson wanda ya kai ziyara a Kyiv a ranar Juma’a ya fitar da tsare-tsare huɗu na samar da makamai da kuma bayar da agaji ga tattalin arziki Ukraine.

Mista Johnson ya ce, burin Shugaba Putin na Rasha ba zai tsaya kawai a tarwatsa Ukraine ba kaɗai.

Shugaban sashen siyasa na ƙungiyar NATO, Jens Stoltenberg ya bayyana cewa akwai buƙatar a ci gaba da kai wa Ukraine ɗauki ko da a ce kuɗin da za a kashe suna da yawa idan ba haka ba Mista Putin zai ci gaba da abin da yake yi.

A bidiyon da ya yi na baya-bayan nan, Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa Rasha ba ta da isassun makamai masu linzamin da za ta iya tarwatsa Ukraine baki ɗaya. In ji BBC.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp