fidelitybank

Za a fuskanci matsananciyar Yunwa a Najeriya – MDD

Date:

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya, mai lura da al’amuran jin ƙai ya yi hasashen samun matsananciyar yunwa a Najeriya da wasu ƙasashen Afirka.

Cikin wani saƙo da ofishin ya wallafa a shafinsa na X, ya yi gargaɗin samun tsanantar matsalar a Najeriya tsakanin watan Nuwamban 2024 zuwa watan Mayun 2025.

”Ya kamata a ɗauki matakai domin yaƙi da yunwa da ceto rayukan mutane a yanzu da kuma tsawon lokaci a nan gaba”, kamar yadda ofishin ya wallafa.

Kauce wa Twitter
Ya kamata a bar bayanan Twitter?
Wannan labari ne na dauke da bayanai da Twitter suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Twitter da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Bayanan da ofishin ya fitar sun nuna cewa a NAjeriya, mutum miliyan 38 ne za su fuskanci matsalar, yayin da ƙasar Sudan ta Kudu ke biye mata da mutum miliyan 21, sai ƙasar Ethiopia mai mutum miliyan 15.

A farkon wannan shekarar ne dai gwamnatin Najeriya ta sanar da wasu matakai uku na kawo sauƙi ga matsalar ƙarancin abinci a ƙasar.

Ɗaya daga cikin matakan shi ne, gwamnatin ta fito da tan 42,000 na abinci daga rumbunan ma’aikatar harkokin noma da nufin kawo sauƙi ga al’ummar ƙasar.

Haka kuma gwamnatin ta ce idan har matsalar ta faskara za ta iya ɗaukar matakin shigar da abinci daga ƙasashen waje domin magance tsadar abinci a faɗin ƙasar

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp