fidelitybank

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Date:

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na iya fuskantar katsewar wuta daga ranar Litinin, yayin da kamfanin rarraba wutar Lantarki na Najeriya (TCN), zai fara aikin gyare-gyaren a layin wuta na Omotosho zuwa wani yanki na Ikeja West.

A cikin wata sanarwa, TCN ya bayyana cewa hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta Najeriya (NERC) da kuma Hukumar tsarin rarraba Wuta ta Ƙasa (NISO) ne suka amince da gyare-gyaren.

“Gyaran zai haɗa da shimfiɗa wasu wayoyi na wutar a layin wutar lantarki na Omotosho/Ikeja wanda aka shirya farawa daga ranar 28 ga Yuli, 2025 zuwa 21 ga Agusta, 2025 daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma,” in ji sanarwar da shugabar hulɗa da Jama’a na TCN, Ndidi Mbah, ta fitar.

Ta kara da cewa bayan kammala aiki a kowace rana, za a maido da wuta ta wannan layi, kuma sauran layukan zasu ci gaba da aiki domin tabbatar da cewa Legas na samun isasshen wuta.

Haka kuma, kamfanonin rarraba wutar lantarki na Eko da Ikeja sun shaida wa abokan cinikayarsu cewa za a fuskanci “yawan katsewar wuta lokaci-lokaci” a lokacin aikin.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp