fidelitybank

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Date:

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na iya fuskantar katsewar wuta daga ranar Litinin, yayin da kamfanin rarraba wutar Lantarki na Najeriya (TCN), zai fara aikin gyare-gyaren a layin wuta na Omotosho zuwa wani yanki na Ikeja West.

A cikin wata sanarwa, TCN ya bayyana cewa hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta Najeriya (NERC) da kuma Hukumar tsarin rarraba Wuta ta Ƙasa (NISO) ne suka amince da gyare-gyaren.

“Gyaran zai haɗa da shimfiɗa wasu wayoyi na wutar a layin wutar lantarki na Omotosho/Ikeja wanda aka shirya farawa daga ranar 28 ga Yuli, 2025 zuwa 21 ga Agusta, 2025 daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma,” in ji sanarwar da shugabar hulɗa da Jama’a na TCN, Ndidi Mbah, ta fitar.

Ta kara da cewa bayan kammala aiki a kowace rana, za a maido da wuta ta wannan layi, kuma sauran layukan zasu ci gaba da aiki domin tabbatar da cewa Legas na samun isasshen wuta.

Haka kuma, kamfanonin rarraba wutar lantarki na Eko da Ikeja sun shaida wa abokan cinikayarsu cewa za a fuskanci “yawan katsewar wuta lokaci-lokaci” a lokacin aikin.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp