fidelitybank

Za a fara shari’ar tsohon Akanta na kasa

Date:

A yau ne hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta EFFCC, za ta gurfanar da tsohon Akanta Janar na kasar Ahmed Idris a gaban wata babbar kotu a Abuja, domin fara yi masa shari’a kan zargin almundaha da hukumar ke yi masa.

Kakakin hukumar ta EFCC, Wilson Uwujaren ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja babban birnin kasar.

Mista Uwujaren, ya ce za a gurfanar da tsohon Akantan tare da wasu mutum uku, bisa zargin sama-da-fadi da kudi sama da naira biliyan 109.

Sauran mutum ukun da ake zarginsa da su, su ne Godfrey Akindele, da Mohammed Usman sai kuma kamfanin Gezawa Commodity Market and Exchange Limited.

Cikin watan Mayun da ya gabata ne dai EFCC ta kama babban Akanta Janar na kasar bayan ya ƙi amsa gayyatar da hukumar ta rinƙa aika masa domin tuhumarsa kan zarge-zargen da ake yi masa, kamar yadda hukumar ta bayyana.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp