fidelitybank

Za a fara sayar da kayan abinci mai rahusa a Legas

Date:

Gwamnatin jihar Legas za ta buɗe kasuwannin sayar da abinci a faɗin jihar..

Kauwannin za su riƙa sayar da kayan abincin a cikin farashin mai rahusa.

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Gbenga Omotoso, shi ya bayyana cikin wata sanarwa a ranar Juma’a.

Ire-iren abincin da za a sayar da ɗin sun haɗa da shinkafa, wake, gari, burodi, kwai, tumatir da kuma borkono, inda Gbenga ya ce za a yi ragin kashi 25.

“Domin tabbatar da cewa kayan abincin ya kai ga illahirin ƴan jihar Legas da kuma kaucewa ɓata-gari shiga ciki, za a ɓullo da wani tsari na bayar da tikiti domin sanin duk waɗanda suka saya,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma ce an zaɓi masu harkar abinci na musamman domin gudanar da shirin.

“Za a riƙa sayar da buhun shinkafa mai nauyin kilogram biyar kan N5,325 yayin da mai nauyin kilogram ɗaya kuma za a sayar kan N1,065, buhun wake mai kilogram biyar N6,225 yayin da mai nauyin kilogram ɗaya kuma N1,245. Za mu sanar da farashin sauran kayan abincin su ma yayin buɗe kasuwannin,” in ji Gbenga.

Ya ce za a buɗe kasuwannin ne a wurare 27 a Ikeja, shida a Legas Island, tara a Ikorodu, biyar a Epe, sai kuma goma a yankin Badagry.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp