A ranar Asaba ne hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB, ta sanar da sayar da fom din shiga manyan makarantun gaba da sakandire (UTME).
Ta shawarci masu neman gurbin shiga jami’a, polytechnic da sauran manyan makarantu da su fara aikin rajistar.
Ta bukaci masu sha’awar shiga da su karbi fom dinsu daga ranar Asabar 14 ga watan Junairu, 2023, inda ta kara da cewa ranar rufe rajistar ita ce 14 ga Fabrairu, 2023.
Hukumar ta ce takardar ta kuma shafi daliban kasashen waje da ke cibiyar rajistar JAMB da ta amince.
Ya shawarci ‘yan takara su buɗe sabon imel ko samun ingantaccen asusun imel ɗin da ke akwai kafin su fara aikin.
Masu neman shiga jami’a, polytechnic da kwalejin ilimi, ana buƙatar samun digiri biyar a O’level, tare da Ingilishi da Lissafi a matsayin tilas.