Hukumar shirya jarabawar kammala sakandire ta yammacin Afrika (WAEC), a Najeriya karkashin jagorancin, Mista Patrick Areghan, ta sanar da cewa, a shirye ta ke ta fara gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WASSCE).
A cewar Mista Patrick Areghan, shugaban ofishin na kasa, a wata zantawa da manema labarai a shelkwatar hukumar, Yaba a ranar Litinin, jarrabawar WASSCE) za ta fara ne a ranar 16 ga Mayu, kuma za ta kare a ranar 23 ga Yuni, 2022 a Najeriya, wanda zai dauki tsawon makonni shida.
Hakan na nufin cewa Hukumar Jarrabawa ta Afirka ta Yamma (WAEC) da kasashe mambobi daban-daban, banda Ghana, yanzu sun sake samun matsaya guda dangane da kalandar karatunsu.