fidelitybank

Za a fara biyan ƴan NYSC alawus ɗin 77,000 daga watan Febrairu

Date:

Shugaban hukumar kula da matasa masu yiwa ƙasa hidima NYSC, Birgadier Janar Yushau Ahmed ya ce za a fara biyan matasan alawus din naira 77,000 daga watan Fabrairun 2025.

Shugaban hukumar ya faɗi hakan ne a jihar Katsina a lokacin da yake yi wa sabbin matasan da aka ɗauka na rukunin ‘C’ jawabi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Yushau ya tabbatar da cewa ƙarin alawus ɗin na cikin kasafin kuɗin ƙasar na shekarar 2025 kuma zai fara aiki ne da zarar an amince da kasafin kuɗin.

“Wannan watan na Janairu ya riga ya ƙare, amma da zarar an amince da kasafin kuɗin a watan Fabrairu mai kamawa, za ku fara karɓar naira 77,000 a maimakon 33,000 da ake biya yanzu,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa matasan cewa ba za a aika su yankunan da babu tsaro ba.

A ranar 25 ga watan Satumban bara ne dai gwamnatin ƙasar ta sanar da yi wa ƴan bautar ƙasa ƙari a alawus ɗin su zuwa naira 77,000 da zai soma aiki daga watan Yulin da ya gabata, wanda aka yi saboda ƙarin mafi ƙanƙantar albashi da gwamnatin ta yi.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp