Shugaban hukumar kula da matasa masu yiwa ƙasa hidima NYSC, Birgadier Janar Yushau Ahmed ya ce za a fara biyan matasan alawus din naira 77,000 daga watan Fabrairun 2025.
Shugaban hukumar ya faɗi hakan ne a jihar Katsina a lokacin da yake yi wa sabbin matasan da aka ɗauka na rukunin ‘C’ jawabi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Yushau ya tabbatar da cewa ƙarin alawus ɗin na cikin kasafin kuɗin ƙasar na shekarar 2025 kuma zai fara aiki ne da zarar an amince da kasafin kuɗin.
“Wannan watan na Janairu ya riga ya ƙare, amma da zarar an amince da kasafin kuɗin a watan Fabrairu mai kamawa, za ku fara karɓar naira 77,000 a maimakon 33,000 da ake biya yanzu,” in ji shi.
Ya kuma tabbatar wa matasan cewa ba za a aika su yankunan da babu tsaro ba.
A ranar 25 ga watan Satumban bara ne dai gwamnatin ƙasar ta sanar da yi wa ƴan bautar ƙasa ƙari a alawus ɗin su zuwa naira 77,000 da zai soma aiki daga watan Yulin da ya gabata, wanda aka yi saboda ƙarin mafi ƙanƙantar albashi da gwamnatin ta yi.