fidelitybank

Za a fara biyan masu yi wa ƙasa hidima sabon alawus na dubu 77

Date:

Kakar masu yi wa ƙasa hidima wato NYSC za ta yanke saƙa a Najeriya, bayan da gwamnatin tarayya ta yi alkawarin biyan su cikon alawus mafi ƙaranci na watannin baya da ba a biya su ba.

Ko da yake babu takamaiman ranar da za a fara biyan matasan masu yi wa ƙasa hidima, amma ministan ci gaban matasa, Ayodele Olawande ya bayar da tabbacin biyan cikon a lokacin da yake magana da gidan talabijin na Channels a ranar Talata.

Tun a watan Satumban 2024 ne gwamnatin ƙasar ta amince da biyan su sabon alawus mafi ƙaranci na naira 77,000 daga naira 33,000 da ake biyan su, sai dai kawo yanzu ba su kai ga cin gajiyar ƙarin ba.

Haka kuma a watan Maris da muke ciki ne ake sa ran masu yi wa ƙasa hidimar za su fara ƙarban sabon alawus din.

Hakan na zuwa ne yayin da miliyoyin ƴan ƙasar ke fama da tsadar rayuwa sakamakon hauhawar farashin kayayyaki saboda janye tallafin man fetur da wasu manufofin da gwamnati ta fito da su.

Lamarin da ya sa wasu masu sharhi ke ganin ƙarin alawus ɗin bai taka kara ya karya

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp