fidelitybank

Za a fara allurar cutar ƙyandar Biri a Najeriya yau

Date:

A yau Litinin ne za a fara allurar riga-kafin ƙyandar biri a wasu jihohi bakwai a Najeriya., wanda hakan zai sa ƙasar ta zama ta uku da za ta yi riga-kafin bayan Rwanda da Jamhuriyar Dumukuraɗiyyar Kongo.

Wannan shi ne karon farko da Najeriya za ta yi riga-kafin a kan cutar ta ƙyandar biri bayan ɓarkewarta.

Ma’aikatar lafiya ta ƙasar ta ce za a fi mayar da hankali ne a kan ma’iakatan lafiya da sauran rukunan jama’a da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar.

A watan Agusta Najeriya ta karɓi allurarn riga-kafin na farko da aka bai wa Afirka, wanda kuma a wannan watan ne hukumar lafiya ta duniya ta ayyana cutar a matsayin annoba ta duniya

Amurka ta bai wa Najeriya kwalaban allurar sanfurin Jynneos (MVA), 10,000.

Tun daga farkon shekarar nan rahotanni sun tabbatar da mutum 118 a jihohi 28 daga cikin 36, da kuma Abuja. ne suka kamu da cutar a Najeriya, kamar yadda hukumar lafiya ta duniya, WHO ta sanar.

Hukumar yaki da bazuwar cutuka ta Najeriya ta ce, zuwa yanzu a wannan shekara daga watan Oktoba, 27, akwai mutane 1,442 da ake zargin sun kamu da cutar daga jihohi 36 da kuma Abuja.

Kasashen Afirka 20 sun tabbatar da bullar cutar a kasarsu a wannan shekara, kuma aranar Asabar ne Angola ta bayar da rahoton mutum na farko da ta tabbatar ya kamu a kasarta.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp