fidelitybank

Za a daɗe a na tuna Malam Argungun Gero – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya aike da ta’aziyyarsa ga iyalai da ‘yan uwa da abokai da mabiyan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Abubakar Giro Argungu, wanda ya rasu ranar Laraba.

Shugaba Tinubu ya bayyana mutuwar malamin da babban rashi ga ƙasar baki ɗaya, sakamakon irin gudunmowar da yake bayarwa wajen yaɗa ilimin addinin musulunci da gyaran tarbiyya ga ƙasar.

“Za a daɗe ana tunawa da Sheikh Giro Argungu a ƙasarnan sakamakon shekarun da ya ɗauka yana yaɗa ilimin addini a ƙasar”, in ji Tinubu, cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ya fitar.

Ayyukan Malamin ta hanyar ƙungiyar JIBWIS, inda ya kasance shugaban kwamitin gudanarwa na ƙungiyar – sun taimaka wajen ilimantar da matasan Musulmin ƙasar.

Tinubu ya ce, za a daɗe a na tuna malamin kan irin tsoron Allah da tawali’unsa da yadda yake kiran shugabanni a matakai daban-daban wajen sauke nauyin talakawa da ya rataya a wuyansu.

Daga ƙarshe shugaban ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalai, da gwamnatin jihar Kebbi da musulman Najeriya, kan wannan babban rashi, tare da yin addu’ar samun gafara shehin malamin

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp