Gwamnatin Saudi Arabia sun kara gyara dokoki ga mahajjata a Makkah da Madinah ta hanyar samar da sabbin matakai, wanda aka gabatar wa al’umma a ranar Asabar.
Kamar yadda gwamnatin ta fada, mahajjatan da suke tahowa daga masarautar ko daga sauran kasashe, ana ganin su na amfani da ababen hawa yayin kiran sallah ( Adhan), wanda hakan bai dace ba, kuma haramun ne, The Islamic Information ta rawaito.
Saboda haka ne, hukumomin Saudi suke jan kunnen al’umma a kan wasa ko kara sautin waka a cikin gidajen dake anguwanni yayin Adhan da Iqamah ( kiran sallah na farko da na biyu).
Daga yanzu duk wanda aka kama ya kunna kowanne irin waka yayin da masallatai suke kiran sallah za a ci shi tarar Riyal 1000 idan wannan shine karon na farko, amma idan ya sake, za a ci shi taran Riyal 2000 saboda sake karya doka.